1. main content
  2. main navigation
  3. extra content
  4. head navigation
  5. search
  6. Choose form 30 Languages

 
 
 

 

 | 03.12.2008 | 17:00 UTC

Rikici tsakanin Indiya da Pakistan

Gwamnatin ƙasar Indiya tayi tsaye kan bakanta, a game da zargin Pakistan da hannu a cikin hare- haren da suka rutsa da birnin Bombey makon da ya gabata.

Hukumomin Pakistan, sun jaddada wannan zargi, albarkacin ziyara da sakatariyar harakokin wajen Amurika Condolisa Rice ta kai a birnin New Delhi, da zumar sasanta ɓangarorin biyu.

Indiya tace  ta na da cikkakar shaida, mai tabbatar da hannu Pakistan a cikin harin, a game da haka, gwamnatin zata ɗauki matakan riga kafi, kamar yadda Pranab Mukherjee Ministan harakokin wajen ƙasar ya nunar:

"Gwamnatin Indiya ta ɗauri aniyar kare al´ummominta da iyakokinta.

Don cimma wannan buri, zamu yi amfani da dukkan matakan da suka dace, kuma muna kira ga ƙasashen ƙetare su bamu haɗin kai a wannan yaƙi da ´yan ta´ada".

Sakatariyar harakokin wajen Amurika, ta buƙaci Indiya tayi takatsantsan,a game da zargin da take wa Pakistan.



 
Picture of the Day
ImageOfTheDay

DW-TV EUROPE live

Kick off! Report - Kick off! Report